POLITICS: President Jonathan writes letter to key Northern citizens (read)

0
247
Reading Time: 6 minutes
By William Oyo-Ita  25 March 2015 10;34


   President Jonathan has written a letter to prominent northern citizens across the 19 states in the region and the FCT. The 2-paged letter (personally signed by the President) is in both English and Hausa versions.

 ENGLISH VERSION

March 23, 2015

My dear Arewa brothers and sisters,

I write you today as President and a firm believer in the value and
significance of the strategic political alliance between the
South-South geo-political zone and the three geopolitical zones in the
Northern part of our country. In my every act as President of Nigeria,
I have been consistently driven by a total commitment to ensuring the
nurturing of this age-old alliance in the larger interest of our dear
nation’s enduring peace, stability, growth and development.

I do understand that my first duty to you, at this time, is to rid the
entire North of the menace of Boko Haram and secure your lives and
property. You and I know that nothing in Nigeria’s past prepared us
for the unprecedented reign of unmitigated terror, mayhem and
destruction which these murderous terrorists have visited on parts of
our country. The initial slowness in effectively responding to this
threat was a result of both the asymmetrical nature of the war on
terror and the need for us to properly equip our security agencies for
the successful prosecution of the war.

Given the recent successes recorded by our armed forces, with your
cooperation and patriotic support, the cooperation of our neighbours,
as well as the laudable gallantry of the men and women of our security
agencies, I am confident that, in the shortest possible time, the
menace of Boko Haram would have been eliminated for good.

My brothers and sisters, your pain is my pain; while there is no way
to replace life, we must find ways to soothe the pains of our fellow
Nigerians and rebuild the lives of persons and communities affected by
these brutal murderers. The painful case of our daughters abducted
from Chibok continues to ache my heart. I assure you that I will not
relent until these innocent girls are rescued and reunited with their
families. While commending you for your prayers, I am confident that,
with the help of Almighty Allah, we will totally defeat and put to
shame these evildoers and their collaborators.

I am sure that you share with me the belief that, without the will of
God, in Whose Hands power resides, I would never have been your
President nor will I continue to be so in the future. Because Nigeria
is today in desperate need of stability, I plead with you to join me
in building on the foundation of the traditional alliance between us
which has always served to keep Nigeria one strong, united and
prosperous nation. My loyalty to my boss, late President Yar’Adua, and
the greatness of the Arewa/South-South alliance under him, is a
well-known testimony to this tradition.

In the past four years, I have remained faithful to our old alliance
especially the appointments of your sons and daughters to high
political offices. In addition, I have worked hard to reverse the over
30 years neglect of Agriculture in Northern Nigeria; address the
challenge of Education through the establishment of dedicated Almajiri
schools and the establishment of Universities in the nine Northern
States that did not have Federal Universities; reduce the death rate
of mothers and babies during birth; give loans to start-up businesses;
restore abandoned irrigation and hydro-power projects; repair the bad
roads and re-build the railway system which is the most viable access
for your goods to the rest of Nigeria and the world.

With gratitude to God, I ask you for the chance to rebuild the North
East, restore the economy and grains pyramids of Northern Nigeria so
that these trains we just brought back can carry your bags of grains
to Lagos, Port Harcourt and Onitsha. My vision and commitment is not
to just move the grains but to also process our agro produce in the
North of our country. It is impossible for me to achieve these great
things if you do not support me and worse still if you refuse to work
with me.

I urge you to disregard the politicians who abuse my person and cause
hatred against my government by telling lies that I denied Arewa power
and am arming Boko Haram. This government that I head means well for
this country. I am committed to the development of the North. I am
totally committed to the unity of this country. 2019 is just four
years away and it is only with the PDP that the vision of rotating
power to the North can be guaranteed. I urge you to stand with the
PDP. I pray that you recall where we are coming from and how I became
President in the first instance. Weigh what your younger generations
under PDP can offer you in the already approaching 2019. Only the PDP
can offer a safe 2019 power shift to the North.


May God Almighty bless you and may God continue to bless the Federal
Republic of Nigeria.


GOODLUCK EBELE JONATHAN




HAUSA VERSION

March 23, 2015

As-salamu Aalaikum Yan’uwana Arewa,

Bayan gaisuwa da fatan alheri. Bayan haka. Gashi lokacin zabubbuka ya
sake zuwa, kuma zabe shine ginshikin dorewar kowane tsarin
demokaradiyya. Ina fatan za mu yi zabe lafiya kuma cikin gaskiya da
adalci.

Tarihi ya nuna yadda yankin arewacin Nigeriya ya zama abokin tafiyar
yankinmu na kudu-maso-kudu. Kun san yadda aka zabi Marigayi Senator
Melford Okilo a cikin majalisar wakilai ta tarayya a jamhuriya ta
farko, wanda kuma goyon bayan da ya baiwa jam’iyyar NPC ta Marigayi
Sardaunan Sakkwato ne ya baiwa jam’iyyar rinjaye a cikin majalisar har
ta kafa gwamnatin tarayya a jamhuriyar. Wannan tarihi ya ringa
maimaita kansa har a jamhuriyya ta biyu. Fata na shine wannan
kyakkyawar dangantakar siyasa dake tsakaninmu zata dore a wannan
lokaci da kuma har abada.

Na rubuto muku wannan takarda ne a matsayina na shugaban kasa domin na
kyautata wannan kyakkyawar dangantakar dake tsakanin yankunan mu tare
da tabbatar da tagomashinta. Wannan shine zai tabbatar da zaman lafiya
da ci gaban siyasa a kasarmu.

Babban aiki na a matsayina na shugaban kasa shine kare rayuka da
dukiyoyin al’uma. Dukkaninmu, ba ma jin dadin abubuwan dake faruwa a
fannin tsaro a kasar nan. A gaskiya babu wanda ya taba tunanin faruwar
irin wadannan abubuwa. Mutanenmu na arewa suna cikin mummunan halin
rashin tsaro sakamakon aiyukan ‘yan ta’adda. Rayuka da dukiyoyi sun
salwanta a sakamakon wannan rikici. Babu wanda ya fi ni bacin Rai da
damuwa akan wannan. To amma, Alhamdulillahi. Yanzu gwamnati ta samar
da managartan kayan fada da makamai ga sojojinmu, kuma muna kara samun
nasara a wannan fada da makiya arewa da Nigeriya. Wadannan nasarori
sun samu ne sakamakon aiki tukuru na sojojinmu, da hadin-kan kasashe
makwabtanmu; uwa-uba kuma da irin addu’oi da goyon-bayan ‘yan kasa na
gari, irinku. Da yardar Allah ba da dadewa ba za mu ga bayan matsalar
“Boko Haram”.

An yi hasarar rayuka a wannan rikici. Sai dai mu yi addu’ar Allah Ya
jikansu, Ya baiwa iyalai da danginsu hakuri, Ya musanya musu da
mafificin alheri. Wanda ya mutu ba ya dawowa. Sai dai mu ci gaba da yi
musu addu’ar neman gafara. Garkuwa da ‘yan ta’adda suke yi da
‘ya’yanmu ‘yan matan Chibok, abu ne mai matukar sosa-rai. Abin ya kan
hana ni barci da sukuni. Duk mutumin kirki, abin ya dame shi. Ina
addu’ar Allah Ya sa suna nan da ransu. In Allah Ya yarda, zan yi duk
abin da zan iya yi domin ganin an kubutar da su lafiya. Ina fatan za
ku taimaka a wannan kokari. Gwamnati tana shirin tsara wani gagarumin
shirin rage radadi, wahala da hasarar da mutane suka yi a yankunan da
ake fama da wannan rikici.

Dukkanninmu mun san mulki na Allah ne. Ya kan bayar ga wanda Ya so.
Zama na shugaban kasa kaddara ce daga Ubangiji. Haka kuma sake cin
zabe na a wannan karo (In Sha Allah), yana hannun Allah. Malamai sun
ce alkalami ya riga ya bushe. Babban abin da kasarmu take so shine
zaman lafiya da kwanciyar hankalin siyasa. Wancen kawancen siyasa da
na fara baiyanawa a cikin wannan takarda tsakanin arewaci da
kudu-masu-kudancin Nigeriya, shine ginshikin daidaita harkokin
siyasarmu. Magabatanmu sun aza harsashin dorewarsa, mu na fatan mu
dora akan abubuwan da suka yi. Zaman lafiya, da biyayyar da na yi wa
Marigayi shugaba Umaru Musa ‘Yar’aduwa wata kyakkyawar alama ce dake
nuna karfin wannan alakar siyasa a tsakanin yankunanmu.

A duk tsawon lokacin mulkina, na tabbatarwa da arewa hakkokinta,
musamman ta fannin nade-naden jami’an gwamnati da habaka aikin noma da
kyautata ilmin Al-Qur’ani ta hanyar kyautata ilmin almajirai, da
kyautata lafiyar mata masu juna-biyu da rage mace-macen mata masu
nakuda da kula da lafiyar jariransu da bayar da bashin kananan sana’oi
da kyautata noman rani da hasken wutar lantarki; uwa-uba ga giggina
sabbin hanyoyi da gyara wadanda suka lalace da farfado da safarar
jiragen-kasa tsakanin arewaci da kudancin Nigeriya. Duk wadannan
aiyuka, na yi ne domin ci gaban arewa da kyautata rayuwar ‘yan uwana
mazauna yankin.

Wadannan aiyuka, kadan ne daga cikin wadanda gwamnatina ta gudanar a
arewa, kuma wata alama ce dake nuna “Juma’ar da zata yi kyau”, idan na
sake cin zaben nan da za a yi a wannan mako. Don haka nake neman
taimakonku da gudunmowarku domin na samu nasara. Akwai gagarumin aiki
a gabanmu, musamman farfado da tattalin arziki da sake gina jihohin
arewa-maso-gabas. Ina sake rokonku ku tallafa min ta duk hanyar da
zaku iya domin tabbatar da ganin Allah Ya bani nasara. Nasara ta, zata
tabbatar da dorewar dangantakar siyasar dake tsakanin yankunanmu, kuma
zata kara tabbatar da hadin-Kan Nigeriya.

Ba gaskiya ba ne, surutan da wasu ‘yan adawa suke yi cewa ni ne na
hana mulki ya dawo arewa. Ba gaskiya ba ne. Jam’iyyar PDP ita kadai ce
take da tsarin da mulki zai komo arewa a cikin shekarar 2019. Kuma na
yi maku alkawarin jam’iyyar zata tabbatar da wannan manufa idan Allah
Ya kai mu lokacin. Hausawa kan ce Mahakurci, Mawadaci. Kuma
Yau-da-gobe mai karyata Boka. Mu kara hakuri, mu kare dangantakar
siyasar dake tsakanin yankunanmu domin arewa ta ci moriyarta a
lokacin.

Daga karshe, ina sake neman goyon-bayanku da taimakonku, da addu’arku
domin ganin na cinye wannan zabe da gagarumin rinjaye. Allah Ya yi
mana albarka, Ya kare kasarmu, Ya tabbatar da zaman lafiyarmu, kuma
Allah Ya tabbatar mini da nasara a wannan zabe. Ameen.

NakGOODLUCK EBELE JONATHAN, gcfr
Shugaban Kasa, kuma Babban Kwamandan Askarawan Nigeriya